Israel Ta Kai Hari Kan Matatar Sinadarai Ta Iran Duk Da Kiran Trump Na A Nuna Kame Kai
Rikicin Gabas ta Tsakiya ya kara kamari bayan da Israâila ta kai hare-haren sama kan wata matatar sinadarai a Iran, duk da rokon Shugaban Amurka Donald Trump na a guji kara tsananta rikicin.
Rahotanni sun bayyana cewa hare-haren sun afku ne a wani katafaren cibiyar sinadarai da ke Mahshahr a kudu maso yammacin Iran. Israâila ta ce harin ya kasance wani bangare na matakan da take dauka kan wuraren da take zargin suna da alaka da karfin soja na Iran.
Trump ya bukaci bangarorin biyu su nuna kame kai domin bai wa kokarin diflomasiyya damar samun nasara. Sai dai harin ya kara dagula halin da ake ciki, tare da tayar da fargabar barkewar babban rikici a yankin.
Masana sun gargadi cewa ci gaba da musayar hare-hare tsakanin Israâila da Iran na iya janyo karin rashin zaman lafiya tare da shafar tattalin arzikin duniya, musamman kasuwar man fetur.
Sharhi