Babban Alkalin Jihar Rivers: “Hannuna Sun Ɗaure”; Ya Dakatar da Tsarin Tsige Fubara da Odu
Port Harcourt — Babban Alkalin Jihar Rivers, Mai Shari’a Simeon Chibuzor-Amadi, ya ƙi amincewa da buƙatar Majalisar Dokokin Jihar Rivers na kafa kwamitin mutum bakwai domin binciken zargin manyan laifuka da ake yi wa Gwamna Siminalayi Fubara da Mataimakiyarsa Farfesa Ngozi Odu.
A wata wasiƙa da ya aika wa Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Martin Amaehwule, Babban Alkalin ya bayyana cewa “hannunsa sun ɗaure” sakamakon umarnin kotu da ke hana shi ɗaukar kowane mataki da ya shafi batun tsige gwamnan da mataimakiyarsa.
Majalisar Dokokin ta riga ta yanke shawarar fara tsarin tsige su bisa tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulki na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima). Sai dai Fubara da Odu sun shigar da ƙara a Kotun Babbar Shari’a da ke Oyigbo, inda kotu ta bayar da umarnin wucin-gadi da ke hana Babban Alkalin da Majalisar ci gaba da wannan tsari.
Mai Shari’a Amadi ya kuma bayyana cewa Majalisar ta shigar da ƙara a Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Port Harcourt, don haka, bisa ka’idar doka, dole ne a dakatar da duk wani mataki har sai kotu ta yanke hukunci na ƙarshe.
Ya jaddada muhimmancin bin doka da oda da mutunta umarnin kotu, yana mai cewa wannan ne ginshiƙin dimokiraɗiyya. A halin yanzu, an dakatar da duk wani mataki na tsige Gwamna Fubara da Mataimakiyarsa, yayin da jama’a ke jiran hukuncin kotu.
Sharhi