Nigeria TV Info
Tinubu Ya Sake Jaddada Kudirin Sauya Fannin Lafiya, Ya Fito Da Muhimmancin Magance Matsalar Wutar Lantarki
Abuja, Nigeria â Shugaban Æasa Bola Ahmed Tinubu ya sake nanata kudirin gwamnatinsa na gyara fannin kiwon lafiya a Najeriya, yana mai jaddada cewa babu Éan Æasa da ya kamata ya rasa ransa sakamakon rashin wutar lantarki a cibiyoyin kiwon lafiya.
Shugaban Æasan ya bayyana haka ne a ranar Talata a taron tattaunawar Æasa kan wutar lantarki a fannin kiwon lafiya, wanda aka gudanar a Ladi Kwali Hall, Continental Hotel, Abuja.
Tinubu, wanda sakataren gwamnatin tarayya (SGF), Sanata George Akume, ya wakilta, ya ce Gwamnatin Tarayya tana mai da hankali wajen samar da hanyoyin kirkire-kirkire da dorewa na samar da makamashi domin tabbatar da ba a samu katsewar wuta ba a asibitocin Æasar.
âYau muna fuskantar babban Æalubale da ya shafi kowane Éan Najeriya: matsalar rashin wutar lantarki da ke ci gaba da addabar manyan asibitocinmu da sauran cibiyoyin kiwon lafiyar jamaâa,â in ji Shugaban Æasa.
Ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa gwamnatinsa na da cikakken kudiri wajen samar da tsarin kiwon lafiya na zamani, mai inganci da sauÆin samu, wanda zai iya biyan bukatun dukkan âyan Najeriya.
Sharhi